Isa ga babban shafi
Nijar

Majalisar Dokokin Nijar ta amince da yiwa tsarin zabe gyaran fuska

Majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar ta amince da a aiwatar da wasu gyare-gyare a kundin tsarin mulkin kasar, wanda zasu shafi muhimman al’amuran kasar ciki harda tsarin gudanar da zabe.

Ginin majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar.
Ginin majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar. Alamy
Talla

A karkashin gyare-gyaren, za’a gudanar da zaben shugabancin kasar zagaye na farko, kwanaki 120 kafin karewar wa’adin shugaban da ke kan karagar mulki, a maimakon kwanaki 40, kamar yadda tsarin yake a baya.

Ministan cikin gidan kasar Bazum Mohammed wanda ya wakilci gwamnati a gaban majalisar kasar, ya shaidawa RFI Hausa cewa hakan zai bai wa kotu isasshen lokaci na sauraron karar da duk wata jam’iyya ta gabatar mata, bayan kammala zabe kafin kama aikin sabuwar gwamnati.

01:18

Majalisar Nijar ta amince da yiwa tsarin zabe gyaran fuska

Nura Ado Suleiman

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.