Isa ga babban shafi
Nijar

An sake bude jami’ar Yamai a yau Lahadi

Mako daya bayan rufe jami'ar Yamai dake Jamhuriyar Nijar, saboda boren dalibai, gwamnatin kasar ta sake bude jami'ar a yau Lahadi biyo bayan koken jama’a.

Dalibi guda ya rasa ransa a boren da ya gudana a jami'ar Yamai.
Dalibi guda ya rasa ransa a boren da ya gudana a jami'ar Yamai. actuniger
Talla

Ministan Ilimi Muhammad Bin Oumar ya fadi cikin wata sanarwa cewa matakin sake bude Jami'ar na zuwa ne saboda koke daga jama’ar dake bukatar a sake bude Jami’ar.

Sanarwar na cewa Shugaban kasar Mahammadu Issoufou ya gana da kungiyoyin daliban Jami’ar domin yi musu hudubar tattalin zaman lafiya.

A halin da ake ciki rundunar ‘yan sandan kasar ta ce ana tsare da dalibai uku wadanda ake zargin suna da hannu a rikicin da ya haddasa mutuwar dalibi daya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.