Isa ga babban shafi
Nijar

Kotu a Nijar ta sallami mutane 15 dake tsare don yunkurin juyin mulki na 2015

Wata kotu a kasar Janhuriyar Nijar ta sallami wasu fararen hula 15 da ake tsare dasu bisa zargin hannu  a yunkurin kifar da Gwamnatin Shugaba Muhammadu Isufu a shekara ta 2015.

Shugaba Muhammadu Isufu na kasar Nijar
Shugaba Muhammadu Isufu na kasar Nijar REUTERS/Afolabi Sotunde/Files TPX IMAGES OF THE DAY
Talla

Lauyan mutanen  Ali Kadir ya tabbatar da sakin mutann da yake karewa.

A watan 12 na shekara ta 2015 ne dai Gwamnatin Muhammadu Isufu ta sanar da cewa ta yi nasarar hana juyin mulki, kuma tana tsare da wasu mutane dake da hannu a ciki.

Majiyoyin samun labarai na cewa an sallami mutane 15, amma kuma akwai manyan sojoji 9 da suka hada da jagoran kifar da Gwamnatin Janar Salou Souleymane wadanda har yanzu ake tsare dasu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.