Sojan Nijar 2 ne, 'yan Boko Haram suka kashe a yankin kan iyakarta da Najeriya
A kalla dakarun sojan kasar Jamhuriyar Niger 2 sun rasa rayukansu a cikin wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram a Najeriya suka kai a garin Baroua dake yankin kudu maso gabashin kasar daf da kan iyakarta da tarayyar Nijeriya
Wallafawa ranar:
A gefen guda kuma hukumar bayarda agajin gaggawa ta MDD Ocha a birnin Yamai, ta bayyana cewa, mutane 25 ne daga cikin dubu 87,037 da ambaliyar ruwan sama da aka sheka a watan Yulin da ya gabata ta rutsa dasu a kasar suka rasa rayukansu
duk da cewa kasar ta Nijar na daya daga cikin kasashen dake fama da fari sakamakon karancin ruwan, amma kuma mutane kerasa rayukansu da gidajensu saboda karancin magudanan ruwa da ake fama dasu a manyan biranen kasar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu