Bakonmu a Yau
Bazoum Mohammad shugaban Jam’iyyar PNDS tarayya a Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:58
A jamhuriyar Nijar yanzu haka jam’iyyun siyasa na ci gaba da daura damara domin zabubukan da ake shirin gudanarwa a farkon shekara mai zuwa. To sai dai wasu na zargin gwamnatin kasar da ci gaba da haddasa rabuwar kawuna a cikin jam’iyyun da ke adawa ita.A zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, Bazoum Mohammad, shugaban Jam’iyyar PNDS tarayya da ke kan karagar mulki, sannan minista na musamman a fadar shugaban kasa, ya ce bai kamata ana alakanta rikicin da wadannan jam’iyyu ke fama da shi a wuyan gwmanatinsu ba.