Boko Haram ta cilla karamin yaro cikin mota mai ci da wuta
Tsohon gwamnan jihar Lagos a mulkin soji, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya ya ce, ya samu bayanai kan cewa, mayakan Boko Haram sun cilla wani karamin yaro cikin wata mota da ke kan ganiyar ci da wuta a yayin harin da suka kaddamar a garin Auno na jihar Borno makwanni biyu da suka gabata.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Mawrwa ya bayyana haka ne a yayin zantawa da kafar talabijin ta Channels a ranar Litinin, inda ya ce, mutumin da ya kwankwadi muggan kwayoyi ne kadai zi iya aikata wannan mummunan aikin.
Wata mata ce da ke cikin motar mai ci da wuta, ta cillo danta waje da nufin tsirar da shi, amma mayakan na Boko Haram suka mayar da yaron cikin motar don shi ma ya babbake tare da mahaifiyarsa.
Rahotanni sun ce, a kalla mutane 30 suka rasa rayukansu a yayin wannan kazamin farmakin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu