Isa ga babban shafi
Najeriya

Ku bamu miliyan 1 ko mu kai muku hari- 'Yan bindigar Katsina

Rahotanni daga jihar Katsina ta Najeriya sun ce, wasu ‘yan bindiga sun bukaci mazauna kauyen Akate da ke Karamar Hukumar Batsari da su biya Naira miliyan 1 domin kauce wa fuskantar hare-haren ‘yan bindigar.

'Yan bindiga sun addabi mazauna kauyuka a wasu johohin arewacin Najeriya
'Yan bindiga sun addabi mazauna kauyuka a wasu johohin arewacin Najeriya Daily Trsut
Talla

Majiyoyin sirri sun ce, tuni mazauna kauyen suka fara karbar Naira dubu 1 da 500 daga kowanne mutun guda domin tara kudaden da ‘yan bindigar suka bukata.

Kauyen Akate na cikin wuraren da ba su da karfin kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga a Katsina.

Ko a makwanni biyu da suka shude, sai da ‘yan bindigar suka dirar wa kauyen, inda suka sace tarin dabbobi.

Wasu daga cikin mazauna kauyen sun yi nasarar kwato dabbobinsu bayan sun fatattaki daya daga cikin barayin, sannan suka mika shi ga sojoji.

Wannan al’amarin ne ya fusata ‘yan bindigar har suka nemi mazauna kauyen da su tara musu Naira miliyan 1 domin kauce wa fuskantar farmakinsu.

Kodayake wasu bayanai sun ce, daga bisani ‘yan bindigar sun amince a biya su Naira dubu 700 bayan sun cimma yarjejeniyar rangwame da mazauna kauyen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.