Ba za mu iya korar hafsoshin tsaron Najeriya ba-Fadar Buhari
Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa, ba za ta iya sallamar manyan hafsoshin tsaron kasar ba a yanzu, tana mai cewa, lokacin korar su bai yi ba.
Wallafawa ranar:
Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ya bayyana haka a babban birnin Abuja a yayin kaddamar da wani littafi.
‘Yan jaridu ne suka yi wa sakataren gwamnatin tambaya game da manyan hafsoshin tsaron da wasu ke korafin cewa, sun gaza samar da tsaro a kasar baya ga kuma jimawar da suka yi suna rike fda madafun iko.
A cewar Boss “ Ba haka kawai ake korar mutane ba, akwai hanyoyi kuma na yi amanna cewa,idan lokaci ya yi, za a bi hanyoyin”.
Da dama daga cikin 'yan Najeriya na cewa, hafsoshin tsaron sun gaza magance rikicin Boko Haram da ke addabar yankin arewa maso gabashin kasar, ga kuma matsalar 'yan bindiga da sace-sacen jama'a da ke ci gaba da ta'azzara a sassan kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu