Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya ce kasa ta 2 a duniya inda ake aurar yara mata - UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya ce Najeriya ce kasa ta biyu a duniya da ake aurar da yara mata masu karancin shekaru.

Wasu kananan yara a sansanin 'yan gudun hijira dake garin Yola a arewa maso gabashin Najeriya.
Wasu kananan yara a sansanin 'yan gudun hijira dake garin Yola a arewa maso gabashin Najeriya. AFP/EMMANUEL AREWA
Talla

Asusun na UNICEF ya ce kididdiga ta nuna cewar, kananan yara mata akalla miliyan 23 aka aurar a kasar, wanda hakan ya kawo karshen ci gaban karatunsu.

Wani rahoto da majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ya nuna cewar adadin kananan yara mata da aka aurar a duniya ya kai kusan miliyan 650.

Babban jami’in asusun na UNICEF a Najeriya Bhanu Pathak, ya bayyana hakan a garin bauchi, yayin bikin cika shekaru 30 da kafa hukumar kare hakkin kananan yara ta duniya CRC, da ya gudana a jihar Bauchi.

Wani rahoto da majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ya nuna cewar adadin kananan yara mata da aka aurar a duniya ya kai kusan miliyan 650.

Zalika rahoton ya yi hasashen cewa akwai fargabar aurar da karin wasu kananan yaran miliyan 150, nan da shekara ta 2030.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.