Isa ga babban shafi
Najeriya-Kano

Yan sanda sun ceto kananan yara daga masu safarar mutane

Rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Kano, ta mika wasu kananan yara ga iyayensu, wadanda aka sace, aka kuma saida a Anambra domin ayyukan bauta.

Wadanda ake zargi da satar kananan yara a birnin Kano suna saidawa a jihar Anambra, tare da wasu daga cikin yaran da 'yan sanda suka ceto daga hannunsu.
Wadanda ake zargi da satar kananan yara a birnin Kano suna saidawa a jihar Anambra, tare da wasu daga cikin yaran da 'yan sanda suka ceto daga hannunsu. Daily Trust
Talla

Kwamishinan ‘yan sandan na Kano Ahmed Ilyasu ya ce kananan yaran da shekarunsu ya kama daga 2 zuwa 10, an sace su ne a lukota daban-daban a jihar, inda wasu ma aka sace su tun a shekarar 2014, amma a yanzu aka gano su a jihar Anambra, inda aka saida su.

A halin da ake ciki kuma an kame mutane 8, bisa zarginsu da hannu wajen sata da safarar kananan yaran.

Wakilinmu a Kano Abubakar Isah Dandago ya aiko mana da Karin bayani cikin rahotonsa. Sai a latsa alamar sautin dake kasa domin sauraron cikakken rahoton.

01:37

Yan sanda sun ceto kananan yara daga masu safarar mutane

Abubakar Issa Dandago

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.