Isa ga babban shafi
Najeriya-Birtaniya

'Yan Najeriya sun yi bore a ofishin jakadancin Birtaniya

Gamayyar Kungiyoyin Fararen Hula ta gudanar da gangami a harabar ofishin jakadancin Birtaniya da ke birnin Abuja na Najeriya domin nuna adawa da wani hukunci da wata kotun Birtaniya ta yanke kan Najeriya.

Masu zanga-zangar sun bayyana hukuncin kotun Birtaniya a matsayin yi wa Najeriya damfara
Masu zanga-zangar sun bayyana hukuncin kotun Birtaniya a matsayin yi wa Najeriya damfara Sahara Reporters
Talla

Kotun ta umarci gwamnatin Najeriya da ta biya wani kamfanin tsibirin Ireland, P&ID zunzurutun Dala biliyan 9.6 sakamakon karya ka’idojin yarjejeniyar kwangilar da ke tsakanin bangarorin biyu.

Gamayyar kungiyoyin ta bayyana hukuncin a matsayin damfara kan Najeriya, yayinda masu zanga-zangar dauke da alluna suka yi biris da ruwan saman da ake tafka wa a birnin na Abuja.

Wasu daga cikin allunan na cewa, “ Najeriya da Birtaniya aminan juna ne, ba makiya ba ne”. “ ‘Yan Najeriya miliyan 200 ba su amince da hukuncin Birtaniya ba.” “ Hukuncin Dala biliyan 9.6 damfara ce”.

Wasu alkaluman na cewa, “ Boris Johnson , ka taimaka wa shugaba Buhari wajen yaki da cin hanci.”

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.