Najeriya ta lashe zinare a Morocco
Tawagwar kwallon kafar Najeriya ta mata 'yan kasa da shekaru 20, ta lashe kyautar Zinare a gasar wasannin motsa jiki ta nahiyar Afrika da ke gudana a Morocco.
Wallafawa ranar:
Talla
Najeriya ta samu nasarar ce bayan doke Kamaru da kwallaye 3-2 a bugun daga kai sai mai tsaron raga.
Da fari dai ‘yan matan na Najeriya da Kamaru sun kammala wasan a 1-1, bayan shafe mintuna 120 suna fafatawa, abinda ya kai ga bugun Fanareti.
Najeriya ta taba lashe kyautar Zinare a fagen kwallon kafar mata yayin wasannin motsa jikin nahiyar Afrika a shekarun 2003 da 2007.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu