Bakonmu a Yau
Farfesa Sadiq Alkafwee dangane da batun bayar da belin zakzaky zuwa neman lafiya India
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:31
Wata kotu da ke Kaduna a Nigeria ta bai wa jagoran shi'a na kasar Ibrahim Zakzaky da matarsa belin tafiya kasar India neman magani amma kuma da rakiyar jamian tsaro.Shekaru 3 kenan Zazzaky na rike hannun hukumomin Najeriyar tun bayan wani rikici tsakanin magoya bayansa da babban Hafson sojin kasar a garin Zaria na jihar Kaduna. Dangane da batun belin mun ji ta bakin Farfesa Sadiq Alkafwee na Jamiar Jihar Nassarawa wanda ya dade a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria kan ko yaya ya ke kallon matakin belin saboda rashin lafiya.