Isa ga babban shafi
Najeriya

Kungiyar Shi'a za ta kalubalanci gwamnati a kotu

Yau ne Kungiyar Islamic Movement in Nigeria da aka fi sani da Shi’a za ta shigar da kara a babban kotun tarayya da ke birnin Abuja domin kalubalantar matakin gwamnatin kasar na haramta gudanar da ayyukanta.

Wasu daga cikin mabiya Shi'a a Najeriya
Wasu daga cikin mabiya Shi'a a Najeriya SODIQ ADELAKUN / AFP
Talla

Babban Lauya mai rike da mukamin SAN, wato Femi Falana wanda ya dade yana kare shugaban kungiyar ta Shi’a Ibrahim El-Zakzaky, ya tabbatar da shirin kungiyar na zuwa kotun a yau Alhamis.

Wannan na zuwa ne jim kadan da kungiyar ta bayyana cewa, ta dakatar da zanga-zangar da take gudanarwa wadda ta rikide ta koma tarzoma a baya-bayan nan.

Mai magana da yawun kungiyar, Ibrahim Musa ya ce, sun dakatar da zanga-zangar ce domin bude sabuwar kofar lalubo hanyar samun masalaha tsakaninsu da gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.