Bakonmu a Yau
Sanata Ibrahim Gobir kan farmakin da 'yan bindiga suka kaiwa kauyuka 70 a Sokoto
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:42
Rahotanni daga Sokoto a Najeriya sun ce ‘yan bindiga dauke da makamai sun tashi garuruwa sama da 70 yayin da suka kashe mutane da dama tare da sace musu dukiya da suka hada da dabbobi.Bayanai sun ce akasarin mazauna garuruwan da maharan suka afkawa sun samu mafaka a manyan garuruwa, domin tsira da rayuwarsu.Dangane da harin ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sanata Ibrahim dake wakiltar yankunan da lamarin ya shafa.