Isa ga babban shafi
Najeriya

za a gurfanar da tsohon ministan sadarwar Najeriya Lai Muhamed a gaban Kotu

Hukumar dake yaki da cin hanci ta Najeriya  ICPC,  tace za ta gurfanar da tsohon ministan yada larabai Lai Mohammed a gaban kotu, domin yin bayani kan yadda Hukumar sadarwar kasa ta kashe naira biliyan 2 da rabi na kudaden da gwamnati ta hanyar da bai kama ta ba.Mai magana da yawun hukumar Rasheedat Okoduwa, ta tabbatar da shirin gurfanar da tsohon ministan a shari’ar da aka yiwa Darakta Janar na hukumar sadarwa Ishaq Modibbo Kawu, na kashe kudaden wajen bada kwangilar da ta saba ka’ida.Tuni ICPC ta gurfanar da Kawu da wasu jami’an hukumar sadarwar a gaban kotu, inda ake tuhumar su da laifuffuka 12 ciki harda yaudarar ministan wajen amincewa da wani kamfani mai zaman kan sa domin yin kwangilar.

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya Lai Muhammed
Tsohon ministan sadarwa na Najeriya Lai Muhammed REUTERS/Afolabi Sotunde
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.