Isa ga babban shafi
Najeriya

Rikici ya mamaye zaben 2019 a Najeriya- HRW

Kungiyar Kare Hakkin Bil'adama ta Human Rights Watch ta yi zargin cewa, hare-hare da tashin hankali sun mamaye zaben shugaban kasar Najeriya da ya gudana a wannan shekara, yayinda ta zargi jami’an soji da 'yan sanda da hannu wajen haddasa matsalolin da aka samu.

Human Right Watch ta ce, an samu koma-baya wajen magance rikicin zabe a 2019 idan aka kwatanta da zabukan shekarun baya
Human Right Watch ta ce, an samu koma-baya wajen magance rikicin zabe a 2019 idan aka kwatanta da zabukan shekarun baya The Guardian Nigeria
Talla

Kungiyar ta ce, an samu hare-haren kungiyar Boko Haram da rikicin Fulani makiyaya da manoma da kuma karuwar hare-haren ‘yan bindiga har ma da garkuwa da jama’a a lokacin gudanar da zaben a wasu jihohin kasar.

Kazalika kungiyar ta bayyana cewa, ‘yan bindiga sun dirar wa wasu rumfunan zabe tare da kai farmaki kan masu kada kuri’u da ‘yan jarida da masu sanya ido a zaben musamman a jihohin Rivers da Kano.

Human Right Watch ta caccaki jami’an tsaro musamman ‘yan sanda kan yadda suka yi sakaci wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a yayin zaben na 2019.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.