Isa ga babban shafi
Najeriya

Kamfanin MTN ya kammala biyan tarar naira biliyan 330 a Najeriya

Kamfanin Sadarwa na MTN mallakin Afrika ta Kudu, ya biya kashin karshe na tarar biliyoyin nairar da gwamnatin Najeriya ta yanka masa, a dalilin saba ka’idar rashin yiwa miliyoyin layukansa rijista, ko kuma katse layukan da ba'a yiwa rijistar ba.

Harabar hedikwatar kamfanin sadarwa na MTN mallakin kasar Afrika ta Kudu a birnin Johannesburg.
Harabar hedikwatar kamfanin sadarwa na MTN mallakin kasar Afrika ta Kudu a birnin Johannesburg. REUTERS/Mike Hutchings
Talla

A kashin karshen dai kamfanin na MTN ya biya gwamnatin Najeriya naira biliyan 55, abinda ya bashi damar kammala biyan tarar ta naira biliyan 330 da hukumar kula da sadarwar kasar NCC ta yanka masa a shekarar 2016.

Da fari dai a watan Oktoban 2015 hukumar ta NCC ta yankawa MTN biyan tarar naira Tiriliyan 1 da doriya ne, saboda laifin kin katse layukansa akalla miliyan 5 da ba a yiwa rijista ba, duk da cewa gwamnatin Najeriya ta baiwa ilahirin kamfanonin sadarwar da ke kasar umarnin yin hakan, to amma daga bisani a 2016 aka sassauta tarar zuwa naira biliyan 330.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.