Mayakan Boko Haram sun karbe sansanin soji a Borno
Mayakan Kungiyar Boko Haram sun karbe wani sansanin soji da ke Jihar Borno a yankin arewa maso gabashin Najeriya, kwanaki kalilan da wani hari ya hallaka sojoji biyar, yayinda 30 suka bace.
Wallafawa ranar:
Majiyar tsaro ta ce, mayakan haye akan babura da manyan motoci sun far wa sansanin sojin da ke Magumeri mai tazarar kilomita 50 daga birnin Maiduguri a yammacin jiya Jumma’a.
Mayakan sun shafe tsawon sa’o’i 4 suna cin karensu babu babbaka a sansanin, in da suka kwashe makamai kafin daga bisani a yi nasarar fatattakar su.
Mayakan ne suka fara korar sojojin cikin daji bayan sun yi musu barin wuta. Amma kawo yanzu babu rahoton asarar rayuka a harin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu