Najeriya-Amurka
Sojin ruwan Najeriya sun kame jiragen ruwa dauke da makamai
Rundunar Sojin ruwan Najeriya ta sanar da kama wasu jiragen ruwa guda biyu tare da mutane 19 da ke dauke da makamai kusa da gabar ruwan kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Kwamandan rundunar sojin da ke kula da gabar ruwan, Kwamado Dickson Olisemenegor ya ce sun yi nasarar kama jiragen ne yayin wani aikin sintiri da suke yi tare da takwarorin su na Amurka.
Jami’in ya ce bayan makaman da aka samu a jiragen biyu, an kuma gano cewar jiragen na dauke da danyan mai na sata.
Cikin mutanen da aka kama har da 'yan kasashen Girka guda 3 da dan Amurka guda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu