Isa ga babban shafi
Najeriya

Tambuwal ya lashe zaben Sokoto

Dan takarar Jam’iyyar PDP a zaben kujerar Gwamnan Sokoto, da kuma ke kan Mulki, Aminu Waziri Tambuwal ya lashe zaben Gwmanan jihar karo na biyu.

Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal.
Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal. Daily Post Nigeria
Talla

Gwamnan jihar ta Sokoto ya lashe zaben ne da tazarar kuri’u 341.

Yayin bayyana sakamakon, Shugabar hukumar zaben Najeriya INEC a jihar ta Sokoto, Fatima Mukhtar, ta ce Tambuwal ya samu kuri’u dubu 512,002, yayinda dan takarar APC Ahmad Aliyu, ya samu kuri’u dubu 511,661.

A ranar 9 ga watan Maris da muke ciki, Tambuwal na kan gaba a zaben na Gwamna ne da kuri’u dubu489,558 yayinda Ahmad Aliyu na APC ke da kuri’u dubu 486,145, sai dai a waccan lokacin, an bayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, sakamakon soke kuri’u dubu 75,403 da aka kada rumfunan zabe 136 da ke kananan hukumomin jihar ta Sokoto.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.