Isa ga babban shafi
Najeriya

An kammala yakin neman zabe a Najeriya

Yau ake kammala yakin neman zaben shugaban kasa da na ‘Yan Majalisar Tarayyar Najeriya kamar yadda dokar zaben kasar ta tanada, yayin da manyan ‘yan takarar shugbancin kasar, wato Muhammadu Buhari na APC da Atiku Abubakar na PDP suka karade lungu da sako na sassan kasar da zummar neman kuri’un al’umma.

Manyan 'yan takarar Jam'iyyun PDP da APC a zaben 2019 na Najeriya, Atiku Abubakar da Muhammadu Buhari
Manyan 'yan takarar Jam'iyyun PDP da APC a zaben 2019 na Najeriya, Atiku Abubakar da Muhammadu Buhari RFI Hausa
Talla

Jam’iyyar APC mai mulki za ta kammala yakin neman zabenta a jihar Katsina a yau Alhamis bayan ta gudanar da gangaminta a jiya a birnin Abuja, koda yake shugaban jam’iyyar na kasa, Adams Oshiomhole da madugun jam’iyyar na kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ba su samu damar halartar gangamin ba.

Ana rade-radin cewa, PDP za ta gudanar da nata gangamin wani lokaci a yau a birnin Abuja, amma babu wata kwakkwarar majiya daga bangaren jam’yyar da ta tabbatar da labarin.

Tun a jiya aka zaci cewa, PDPn za ta yi gangamin nata a Abuja, amma ya ci karo da na APC mai mulkin kasar.

A ranar Asabar mai zuwa ne, ake saran kimanin mutane miliyan 84 za su halarci rumfunan zabe a sassan kasar domin kada kuri’unsu ga wanda suke fatan kasancewa shugaban Najeriya a shekarar 2019.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.