INEC ta kara wa'adin karbar katunan zabe
Hukumar shirya zaben Najeriya INEC, ta kara wa'adin ci gaba da karbar katunan zabe na din-din-din da tsawon kwanaki uku.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ranar Juma'a 8 ga watan Fabarairu, hukumar zaben ta tsara kawo karshen raba katunan, wanda a yanzu tace za a ci gaba da rabawa zuwa ranar Litinin, 11 ga watan Fabarairu.
Shugaban hukumar zaben ta Najeriya Farfesa Mahmoud Yakubu, ya ce matakin kara wa'adin, ya biyo bayan koken da jama'a da dama suka gabatar kan bukatar.
Farfesa Yakubu ya kuma ce, ma’aikatan hukumar ta INEC za su gudanar da aikin raba katunan zaben na din-din-din daga karfe 9 na safe, zuwa 6 na yamma a ranakun Asabar da Lahadi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu