Muhallinka Rayuwarka
Dalilan da suke haddasa tsadar kayan abinci a Najeriya duk da karuwar wadanda ke rungumar noma
Wallafawa ranar:
Kunna - 19:59
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan makon ya dora ne kan tattauna bisa batutwa guda 2, da suka hada da ci gaba da bibiyar halin da noma ke ciki a wasu yankunan da ambaliya ta shafa a sassan Najeriya da wadanda basu bata shafa ba, sai kuma alkalumman da gammayar kungiyoyin manoman Najeriya suka fitar dangane da ci gaban da aka samu na karin wadanda ke rungumar noma a baya bayan nan.