Isa ga babban shafi
Najeriya

An kafa dokar hana zirga-zirga a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna da ke tarayya Najeriya ta sanya dokar hana fita na tsawon awanni 24 domin tabbatar da doka da oda a ciki da wajen gari.

Wasu jami'an 'yan sandan Najeriya.
Wasu jami'an 'yan sandan Najeriya. Reuters
Talla

Kakakin gwamnan jihar Samuel Aruwan ya tabbatar da daukar matakin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Ladin nan.

Al’amarin rashin tsaron ya biyo bayan rikicin da aka samu a yankin Kasuwan Magani dake karamar hukumar Kajuru ranar Alhamis 18 ga Oktoba, inda akalla mutane 55 suka rasa rayukansu.

Wakilinmu daga Kaduna Aminu Sani Sado ya aiko mana da rahoto kan halin da ake ciki.

01:27

An kafa dokar hana zirga-zirga a Kaduna

Aminu Sani Sado

A watan fabarairun da ya gabata an taba samun makamancin wannan rikici, a yankin na Kasuwan Magani, inda akalla mutane 10 suka mutu, daga bisani kuma aka kama wasu mutane 65 bisa zarginsu da hannu cikin rikicin, har yanzu kuma shari’ar da ake musu a kotu na ci gaba da gudana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.