Bakonmu a Yau
Tsohon Gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido kan datse kofar shiga majalisar Najeriya da jami'an tsaro suka yi
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:50
Matsalar da aka samu a Majalisar dokokin Najeriya kan yadda jami’an tsaro suka hana Yan Majalisu da ma’aikata shiga Majalisar ranar talata na cigaba da daukar hankalin ‘yan siyasa da masu rajin kare dimokiradiya.Dangane da wannan dambarwa Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma dan takarar shugaban kasa a Jam’iyyar PDP, Alhaji Sule Lamido wanda yanzu haka ke ziyarar sassan yammacin Najeriya, lokacin da ya isa birnin Lagos.