Isa ga babban shafi
Najeriya

Sauyin shekar wasu 'yan majalisu alheri ne ga jam'iyyar APC - Oshiomhole

Shugaban jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, Adams Oshiomhole ya ce ficewar wasu sanatoci da kuma ‘yan majalisar wakilai daga jami’yyar, nasara ce ga a gare ta, sabanin akasin haka da wasu ke gani.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, tare da sabon shugaban jam'iyyar APC, kuma tsohon gwamnan jihar Edo Adams Oshiomhole.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, tare da sabon shugaban jam'iyyar APC, kuma tsohon gwamnan jihar Edo Adams Oshiomhole. Duisaf.com
Talla

Oshiomhole ya bayyana haka ne yayin ganawa da manema labarai a Abuja, bayan ganawarsa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

Sanatoci 15 da kuma ‘yan majalisar wakilai 37 ne suka fice daga cikin jam’iyyar APC, bisa dalilan rashin gamsuwa da ayyuka da kuma manufofin gwamnatin Najeriya a karkashin jagorancin Muhammadu Buhari.

Daga cikin wadanda suka yi sauyin shekar, akwai Rabi’u Musa Kwankwaso mai wakiltar Kano ta tsakiya da Dino Melaye mai wakiltar Kogi ta yamma da kuma Suleiman Hunkuyi daga Kaduna ta Arewa.

Shugaban na APC, Adams Oshiomhole ya bayyana wadanda suka fice daga cikin jam’iyyar a matsayin wadanda ba su amince da kyawawan manufofin da ta sa a gaba ba.

A cewar Oshiomhole, abin farin ciki ne ganin yanzu, za a gina jami’yyar APC mai karfi, da ba za ta zama wani tsani na samun mukaman siyasa ko son zuciya ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.