Adams Oshiomole kan ficewar wasu 'yan majalisun APC zuwa PDP
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:24
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana aniyar sa ta aiki da kowane dan majalisa ba tare da la’akari da Jam’iyyar da ya fito ba, inda ya ce a dimokiradiya kowa na da ‘yancin tafiya inda yake so.Yayin da yake tsokaci kan ficewar wasu daga cikin yan majalisun jam’iyyar sa zuwa Jam’iyyar PDP, Buhari yace wasu daga cikin yan majalisun na da matsala ne da mazabun su, kuma sun yi iya bakin kokarin su wajen ganin basu sauya shekar ba, amma abin yaci tura.Sai dai da alama matsayin shugaban Jam’iyyar ta APC Adams Oshiomhole ya saba da na shugaba Buhari, kamar yadda za a ji a tattaunawarsa da wakilinmu a Abuja, Aminu Manu.