Ba zan gudu daga Najeriya saboda EFCC ba- Fayose
Gwamnan Jihar Ekiti mai barin gado, Ayodele Fayose ya ce, ba zai gudu daga Najeriya ba da zaran wa'adin rigar kariyarsa ya kare a cikn watan Oktoba mai zuwa, yayin da rahotanni ke cewa Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, EFCC ta yi barazanar gudanar da bincike a kansa da zaran ya kammala wa'adinsa.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yawun Fayose, Lere Olayinka ya shaida wa manema labarai cewa, babu abin da gwamnan ke tsoron sa, in da ya ce, “me za a yi ma shi? Shin Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, EFCC ita ce kotun shari'a?”.
A cewar Lere ya gana da gwamnan game da makomarsa ba tare da rigar kariya ba bayan karewar wa’adinsa na gwamnan Ekiti.
A ranar 6 ga watan Oktoba mai zuwa ne ake saran Fayose na jam’iyyar adawa ta PDP ya mika mulki ga Kayode Fayemi da ya lashe zaben gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar APC a ranar Asabar da ta gabata.
Mr. Fayemi ya lashe zaben ne bayan ya yi nasarar doke mataimakin gwamna a EKiti kuma dan takarar PDP, Kolapo Olusola-Eleka.
Jim kadan da ayyana sakamakon zaben a ranar Lahadi, aka fara rade-radin cewa, akwai yiwuwar Fayose ya tsere daga Najeriya don kauce wa gurfana a gaban shari’a da zaran ya mika mulki nan da watanni uku masu zuwa.
Hukumar EFCC ta yi barazanar bincikar Fayose kan zarge-zargen almundahana a wani aikin kiwon kaji a shekarar 2006.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu