Bakonmu a Yau
Shugaban Faransa Emmanuel Macron kan ziyarar da ya kai Tarayyar Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:52
4 ga watan Yuli na shekarar 2018, ita ce rana ta biyu kuma ta karshe a ziyarar da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya kai tarayyar Najeriya.A ranar farko ta ziyarar ce shugaba Macron ya gana da takwaransa Muhammadu Buhari a birnin Abuja, kafin daga bisani ya wuce zuwa Legas domin gudanar da wasu ayyuka.Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da shugaban Emmanuel Macron dangane da wannan ziyara da ya kai a Najeriya, ga kuma zantawarsu.