Buhari zai ziyarci Filato don jajanta wa jama'ar jihar
Rahotanni daga Najeriya na cewa akwai yiwuwar shugaban kasar Muhammadu Buhari ya ziyarci jihar Filato a yau Talata don jajanta wa al’ummarta sakamakon rikicin baya-bayan nan da ya lakume rayukan mutane kusan 100.
Wallafawa ranar:
Jaridar Daily Trust da ake wallafawa a kasar ta rawaito cewa, shugaba Buhari zai yada zango a Filato bayan ya baro birnin Calabar da ke jihar Cross Rivers a yammacin yau.
A wannan safiya ne shugaba Buhari ya kama hanyarsa ta zuwa Calabar daga birnin Abuja don kaddamar da wasu ayyukan gwamnati a jihar.
A jiya ne mataimakin shugaban, Farfesa Yemi Osinbajo ya ziyarci Filato saboda wannan ibtila’in da ya afka ma ta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu