Hon. Hamisu Shira kan amsa tambayoyi da Obasanjo zai yi akan Dala biliyan 16 da ya batar wajen gyara lantarki
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:38
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa tsohon shugaban kasar Olusegun Obasanjo na da tambayoyin da zai amsa kan yadda aka kashe Dala biliyan 16 don gyaran lantarki ba tare da kwalliya ta biya kudin sabulu ba lokacin mulkinsa.Buhari ya bayyana haka ne lokacin ganawa da kungiyar magoya bayan sa a karkashin shugaban hukumar kwastam, Kanar Hameed Ali da ta ziyarce shi.Wannan na zuwa ne bayan da Hukumar SERAP dake neman ganin an aiwatar da gaskiya a Najeriya ta bukaci babban mai shari’ar kasar ya kafa kwamitin bincike kan lamarin.Dangane da haka, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon. Hamisu Shira, tsohon dan majalisar wakilai, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.