Isa ga babban shafi
Najeriya

Ebola: Jami'an Najeriya sun fara sa ido akan lafiyar fasinjoji

Ma’aikatar lafiya ta Najeriya ta dauki matakan shirin ko ta kwana, inda ake na sa ido akan shigi da ficen jama’a a akan iyakokin kasar da kuma filayen jiragen sama, bayan samun rahoton sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Congo.

Wasu jami'an lafiya na kungiyar likitocin kasa da kasa ta Medecins sans Frontieres (MSF), yayin aiki a wata cibiyar kula da masu fama da cutar Ebola, Kailahun da ke kasar Saliyo.
Wasu jami'an lafiya na kungiyar likitocin kasa da kasa ta Medecins sans Frontieres (MSF), yayin aiki a wata cibiyar kula da masu fama da cutar Ebola, Kailahun da ke kasar Saliyo. REUTERS/Tommy Trenchard
Talla

Zuwa yanzu kuma cutar ta Ebola ta yi sanadin mutuwar akalla mutane 17 a kasar.

Ministan lafiya na Najeriya, Isaac Adewole ya ce za a rika bin matakai masu tsauri don tantance fasinjojin da ke shiga kasar, musamman wadanda suka fito daga Jamhuriyar Congo.

Wannan dai shi ne karo 9 da aka sake samun bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Congo, tun bayan fara bayyanarta a shekarar 1976.

A shekarar 2014 ne cutar Ebola ta hallaka kusan mutane 11,000 bayan bullar da ta yi a kasashen Liberia, Saliyo da kuma Guinea.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.