Ebola: Jami'an Najeriya sun fara sa ido akan lafiyar fasinjoji
Ma’aikatar lafiya ta Najeriya ta dauki matakan shirin ko ta kwana, inda ake na sa ido akan shigi da ficen jama’a a akan iyakokin kasar da kuma filayen jiragen sama, bayan samun rahoton sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Congo.
Wallafawa ranar:
Zuwa yanzu kuma cutar ta Ebola ta yi sanadin mutuwar akalla mutane 17 a kasar.
Ministan lafiya na Najeriya, Isaac Adewole ya ce za a rika bin matakai masu tsauri don tantance fasinjojin da ke shiga kasar, musamman wadanda suka fito daga Jamhuriyar Congo.
Wannan dai shi ne karo 9 da aka sake samun bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Congo, tun bayan fara bayyanarta a shekarar 1976.
A shekarar 2014 ne cutar Ebola ta hallaka kusan mutane 11,000 bayan bullar da ta yi a kasashen Liberia, Saliyo da kuma Guinea.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu