Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Legas zata rushe babbar mayankar jihar

Gwamnatin Lagos a Najeriya ta umurci masu sayar da dabbobi a babbar mayakan jihar wato abbatoir da ke Agege, da su tattara nasu ya nasu su bar wurin, domin za a rusa wurin nan ba da jimawa ba.

Wani sashi na babbar mayankar dabbobi ta jihar Legas da ke karamar hukumar Agege, Najeriya.
Wani sashi na babbar mayankar dabbobi ta jihar Legas da ke karamar hukumar Agege, Najeriya. BusinessDay
Talla

Hakan yasa shugabancin ‘yan kasuwar dabbobin suka bukaci masu fataucin shanu daga arewa zuwa Lagos da su dakatar da wannan fatauci har sai abin da halin ya yi.

Har yanzu dai gwamnatin jihar ta Lagos bata kayyade wa’adin da ta debawa masu gudanar da sana’arsu a mayankar ba.

Wannan matakin ne yasa yayin zantawarsa da sashin hausa na RFI, Alhaji Abdullahi Liliga, shugaban Miyatti a jihar ta Lagos, ya bayyana cewa matakin tamkar bita da kulli gwamnati ke nufinsu da shi, kasancewar hatta wurin wucin gadin da ta basu a yanzu kuma ta ce shima rusa shi zata yi.

00:57

Gwamnatin Legas zata rushe babbar mayankar jihar

Abdoulkarim Ibrahim

Bincike ya nuna cewa akalla shanu da sauran dabbobi, 8,000 ne ake yankawa kowace rana Lagos, wadanda aka kiyasta kudinsu zai kai Naira biliyan daya da rabi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.