Za mu yi sahihin Zabe a 2019- Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari ya tabbatar wa Majalisar Dinkin Duniya cewa, Najeriya za ta gudanar da sahihin zaben shugaban kasa a shekarar 2019.
Wallafawa ranar:
Shugaba Buhari ya bada tabbacin ne a yayin ganawarsa da Mataimakiyar Magatakardar Majalisar Dinkin Duniya, Amina Muhammed a birnin tarayya Abuja.
Buhari ya yi marhabin da goyon bayan Majalisar a yayin da kasar ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da zaben a badi.
Amina Mohammed ta zanta da Buhari akan abubuwa da dama da suka shafi zabe da tasa keyar ‘yan gudun hijirar Kamaru da kasuwancin bai daya a nahiyar Afrika da kuma matsalar tsaro a yankin arewa maso gabashin Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu