Isa ga babban shafi
Najeriya

Mèdecins Sans Frontières ta janye jami'anta daga Rann

Kungiyar likitocin kasa da kasa, ta Mèdecins sans Frontières ta ce ta dakatar da ayyukan jami’anta a garin Rann da ke jihar Borno, tare da kwashe su, biyo bayan farmakin da mayakan Boko Haram suka kai inda suka hallaka musu jami’ai 3.

Wani sansanin 'yan gudun hijira a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda jami'an lafiya na kungiyar likitocin kasa da kasa ta Mèdecins Sans Frontières ke ayyukan agaji.
Wani sansanin 'yan gudun hijira a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda jami'an lafiya na kungiyar likitocin kasa da kasa ta Mèdecins Sans Frontières ke ayyukan agaji. Médecins Sans Frontières
Talla

Matakin yana kunshe cikin sanawar da kungiyar likitocin ta Mèdecins sans Frontières ta fitar, inda ta yi Karin bayanin cewa ta janye ma’aikatanta na cikin Najeriya da na waje guda 22.

A ranar Alhamis da ta gabata, mayakan na Boko Haram suka kai wa wani barikin sojojin Najeriya hari a garin na Rann, inda suka hallaka akalla mutane 11, ciki har da ma’aikatan lafiyar na Mèdecins sans Frontières 3.

Har yanzu dai babu tabbacin iyaka yawan wadanda suka hallaka da kuma wadanda harin ya jikkata. Sai dai jami’an agajin na Mèdecins sans Frontières, sun ce sun bai wa akalla mutane 9 kulawa sakamakon jikkatar da suka yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.