Isa ga babban shafi
Turai

Tarayyar Turai za ta bai wa Borno maƙudan kuɗaɗe

Ƙungiyar Tarayyar Turai EU, ta ce za ta miƙa wa gwamnatin jihar Borno da ke arewa maso-gabashin Najeriya kuɗi Yuro miliyan 143, kwatankwacin Naira biliyan 60.

Rikicin Boko Haram ya shafi yankunan da ke gabar tafkin Chadi.
Rikicin Boko Haram ya shafi yankunan da ke gabar tafkin Chadi. STRINGER / AFP
Talla

Kuɗaɗen suna a matsayin tallafi ne ga jihar domin murmurewa daga ɓarnar da rikicin Boko-Haram ya haifar.

Za a yi aiki da maƙudan kuɗaɗen ne a tsawon shekaru 3, wajen samar da wadataccen abinci mai gina jiki ga al'umma, da kula da lafiya, da tsaftar muhalli da kuma samar da ayyukan yi a tsakanin al’ummomin da rikicin Boko Haram ya shafa.

Ofishin bayar da agaji na majalisar ɗinkin duniya ya ce sama da mutane miliyan biyu ne rikicin na Boko Haram ya ɗaiɗaita.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.