Burtaniya za ta aika da jiragen yaƙi zuwa Mali
Burtaniya ta amince za ta aika da jirage masu saukar ungulu zuwa Mali domin taimaka wa dakarun Faransa wajen yaƙi da ayyukan ta'addanci a yankin Sahel na nahiyar Afirka.
Wallafawa ranar:
Wannan mataki na da muhimmanci kasancewar ƙasar ta Faransa na da rauni a wannan fanni, kuma ana kallon hakan a matsayin mafari na kai irin wannan ɗauki a yankin.
An cimma wannan yarjejeniya ce a taron da Firaministan Burtaniya Theresea May da takwaranta na Faransa Emmanuel Macron suka gudanar ranar Alhamis a ƙasar ta Burtaniya.
A nata ɓangaren, Faransa za ta samar da dakaru waɗanda za su tallafa wa dakarun ƙawance na NATO da Burtaniya ke wa jagoranci a ƙasar Estonia.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu