Isa ga babban shafi
Najeriya

Super Eagles za ta fafata da Ingila

To mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Najeriya super Eagles Gernot Rohr ya tabbatar da cewa ‘yan wasan Najeriyar za su fafata da takwarorinsu na Birtaniya a wasannin sada zumunta gabanin wasan cin kofin duniya da zai gudana a Rasha.

Tawagar kungiyar kwallon kafar Najeriya Super Eagles lokacin da suke karbar umarni daga Kocinsu Gernot Rohr yayin wata fafatawa.
Tawagar kungiyar kwallon kafar Najeriya Super Eagles lokacin da suke karbar umarni daga Kocinsu Gernot Rohr yayin wata fafatawa. NFF
Talla

Rohr yayin tattaunawarsa da manema labarai ya ce Super Eagles za ta kece raini da ‘yan wasan na Ingila ranar 2 ga watan Yuli a filin wasa na Wembley da ke birnin London.

Kasashen biyu na Ingila da Najeriya na cikin rukuni na uku a wasannin cin kofin duniya da zai gudana.

Kocin Najeriyar ya ce fafatawar abar alfahari ce kuma dama ce ta yadda ‘yan wasan na Super Eagles za su nuna bajintarsu ga zakarun duniya na 1966.

Tuni dai mataimakin shugaban hukumar kwallon kafa na farko a Najeriya Seyi Akinwunmi ya ce matakin wasan babban ci gaba ne ga Super Eagles.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.