Isa ga babban shafi
Najeriya

‘Yan ta’adda sun jahilci koyarwar Addini - Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, cikin kakkausan harshe, ya caccaki masu hallaka mutane ta hanyar kai hare-haren ta’addanci da sunan jihadi.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. The U.S. | Post-Nigeria
Talla

Buhari ya ce ayyukan irin wadannan masu da’awah ya nuna yadda karara suka jahilci koyarwa ta addini, domin kuwa babu yadda za’a yi Mahalicci yayi da kisan rayukan da basu jib a basu gani ba.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban Najeriyar Malam Garba Shehu ya fitar, Muhammadu Buhari ya bayyana haka ne yayinda a lokuta mabanbanta, yake tataunawa da tawagar shugabancin darikar Qadiriyya na nahiyar Afrika, da kuma na Izalatul Bid’a Wa Iqamatus-Sunna a fadar gwamnati da ke Abuja.

Shugaban ya jaddada cewa jami’an tsaron kasar zasu ci gaba da aiki tukuru wajen bibiya tare da yi wa tsarin samar da tsaro ga rayuka da dukiyar al’ummar kasar garambawul, domin shawo kan dukkanin matsalolin tsaron da ke addabar Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.