Kaduna: 'Yan bindiga sun hallaka Sarkin Gwantu
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe Sarkin Gwantu wato Etum Numana a karamar hukumar Sanga, da ke jihar Kaduna a tarayyar Najeriya.
Wallafawa ranar:
‘Yan bindigar sun kuma hallaka matar Sarkin, yayin da suka yi wa dansa rauni ta hanyar harbi da bindiga.
Lamarin ya faru ne a cikin daren jiya Lahadi, kuma wakilinmu Aminu Manu, ya ziyarci asibiti inda ake jinyar daya dada cikin ‘ya’yan sarkin da ya samu rauni wato Dan Azumi Makama, wanda ya yi masa karin bayani dangane da yadda lamarin ya faru.
Najeriya-Kaduna-Dan Azumi Makama-2018-01-01
Gwmnatin Kaduna ta tabbatar da faruwar wannan lamari, kuma a cewar kakakinta Samuel Aruwan, tuni aka bai wa jami’an tsaro umarnin fara bincike don gano wadanda ke da hannu a kai harin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu