Bakonmu a Yau
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje kan biyan albashin ma'aikata
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:00
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya umurci Gwamnonin kasar 36 da su tabbatar sun biya albashin ma’aikatan da ake bin su kafin bikin kirsimeti da za’ayi a karshen wannan shekara. Buhari ya bayyana haka ne yayin gudanar da wani taro tare da Gwamnonin a fadar sa kan bukatar basu Karin kudaden Paris Club. Wakilinmu a Abuja, Muhammad Kabir Yusuf ya tattauna da Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje bayan kamala taron kuma ga yadda hirar su ta kaya.