Isa ga babban shafi
Najeriya

Mayakan Boko Haram sun hallaka sojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce akalla sojin ta uku ne suka mutu yayinda karin wasu uku kuma suka jikkata a wani hari da mayakan Boko Haram suka kai kansu da yammacin jiya Asabar a garin Magumeri mai nisan kilomita 50 da birnin Maiduguri.

Kafin yanzu dai yankin na Magumeri ya fuskanci hare-hare da ga tsagin kungiyar ta Boko Haram da ke samun goyon bayan kungiyar IS karkashin
Kafin yanzu dai yankin na Magumeri ya fuskanci hare-hare da ga tsagin kungiyar ta Boko Haram da ke samun goyon bayan kungiyar IS karkashin ledernierpoint
Talla

Kafin yanzu dai yankin na Magumeri ya fuskanci hare-hare da ga tsagin kungiyar ta Boko Haram da ke samun goyon bayan kungiyar IS karkashin jagorancin Abu Mus’ab al-barnawi.

Ko a watan Yulin da ya gabata ma akalla mutane 69 ne da suka kunshi sojoji da sauran jami’an tsaro suka mutu a yankin bayan wani farmaki da mayakan suka kai kan kwararru masu binciken albarkatun man fetur.

A cewar kakakin runduna ta 8 ta sojin Najeriya, ko a baya mayakan sun yi yunkurin kai farmaki sansanin sojin da ke Magumeri amma sojin suka dakile yunkurin.

Wata majiyar tsaro a Maidugurin babban birnin jihar Borno, ta shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa, akwai kwakkwaran zaton cewa mayakan sun fito ne daga yankin Dabar Masara wani tsibiri a tafkin Chadi wurin da ne ake tsammanin shi ne maboyar tsagin kungiyar ta Boko Haram da ke biyayya ga Abu Mus’ab al-barnawi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.