Isa ga babban shafi
Najeriya

Hatsarin jirgin kasa ya kashe mutane a Legas

Rahotanni daga birnin Legas da ke kudancin Najriya na cewa, mutane da dama sun rasa rayukansu bayan wani jirgin kasa ya kauce hanyarsa a garin Agege a wannan safiya.

Hatsarin jirgin kasa ya hallaka mutane a birnin Legas
Hatsarin jirgin kasa ya hallaka mutane a birnin Legas STRINGER / AFP
Talla

Mai Magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Olarinde Famous-Cole ya tabbatar da aukuwar lamarin, in da ya kara da cewa, jirgin ya kuma ci karo da wata katuwar motar daukan kaya.

Famous-cole ya ce, a yanzu haka, an tura jami’an tsaro wurin da hatsarin ya faru amma bai bada alkaluman mutanen da suka mutu ba.

Ba a karon farko kenan ba da ake samun hatsarin jirgin kasa a garin Agege mai cike da hada-hadar jama’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.