Isa ga babban shafi
Najeriya

Kotun ECOWAS ta bukaci Najeriya ta biya ‘yan Biafra Diyya

Kotun Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS, ta bukaci Gwamnatin Najeriya ta biya diyyar naira biliyan 88 ga mutanen yankin Biafra saboda gazawa wajen kwance bama-baman da aka jibge a Yankin su bayan kammala yakin.

Shugaban Kungiyar IPOB Nnamdi Kanu
Shugaban Kungiyar IPOB Nnamdi Kanu REUTERS/Stringer
Talla

Alkalin kotun ya umurci gwamnatin ta bada naira biliyan 50 ga mutanen Yankin da suka fito daga Jihohi 11 da kuma bada Karin naira biliyan 38 da za’ayi amfani da su wajen kwance bama-baman da gina makarantu da kotuna da mujami’u da Masallatai a Jihohin.

Tuni dai Najeriyan ta bayyana gamsuwarta da wannan hukunci tare da alkawarta biyan diyyar.

Alkaluma sun ce akalla mutane miliyan guda ne suka mutu a Yakin Biafra na shekaru 3.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.