Isa ga babban shafi
Najeriya

An jibge Jami'an tsaro a Shalkwatar NNPC da ke Abuja

Rahotanni daga Abuja babban birnin Najeriya na cewa, an girke tarin jami’an tsaro da suka kunshi sojoji da ‘yansanda a Shalkwatar kamfanin man kasar NNPC da ke birnin a yau Asabar. Ana dai ganin hakan baya rasa nasaba da takaddamar da ta kunno kai tsakanin Ministan Albarkatun Man kasar Ibe Kachikwu da shugaban kamfanin na NNPC Mai Kanti Baru.

Karamin Ministan Man Fetur na Najeriya Emmanuel Ibe Kachikwu.
Karamin Ministan Man Fetur na Najeriya Emmanuel Ibe Kachikwu. Reuters
Talla

Sai dai a cewar wata majiya daga kamfanin, dama bisa al’ada akwai jami’an tsaron da dama da ke sanya ido a shige da ficen kamfanin kowacce rana, amma dai an kara yawansu a yau sakamakon bayanan da suka samu cewa akwai yiwuwar wasu taron matasa za su gudanar da Zanga-Zanga kan zargin da ake yiwa Shugaban na NNPC Mai Kanti Baru.

Tun da farko dai karamin Ministan albarkatun man fetur din Najeriyar Emmanuel Ibe Kachikwu ne ya aikewa shugaban kasar Muhammadu Buhari da wata takaddar Korafi, inda a ciki ya zargi Baru da cin amanar kasa, baya ga gudanar da wasu harkokin kamfanin da ya kunshi bayar da kwangila ba tare da sanin Mininstan ba.

Sai dai masu sharhi siyasa a kasar na kallon zargin a matsayin wani lamari da ka iya zama bi ta da kulli, ganin yadda shugaban ke tattaunawa kai tsaye da shugaban ba tare da sa hannun Ministan ba.

A jiya Juma'a ne dai Baru ya gana da shugaban kasar Muhammadu Buhari a masallacin fadarsa ta Villa da ke Abuja jim kadan bayan idar da Sallar, sai dai babu cikakken bayanai kan ko sun tattauna dangane da takaddar korafin ko akasin haka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.