Najeriya
An tsinto gawarwaki 16 bayan nitsewar kwale-kwale a Kebbi
An tsinto gawarwaki 16 cikin mutum sama da 50 da kwale-kwale ya nitse da su ranar talatan da ta gabata a garin Yawuri na jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Mutum 57 aka kiyasta na kan kwale-kwalen lokacin da ya nitse, inda aka samu damar ceto rayukan mutum 7 da gawarwaki 16.
A ranar talatan da hatsarin ya auku an gano gawarwaki 15 yayinda a jiya laraba kuma aka tsinto guda.
Masu aikin ceto na ci gaba da bincike sauran gawarwakin.
Wannan ba shine karo na farko da kwale-kwale ke kifewa da fasinjoji a Kebbi ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu