Tsawaita wa’adin dagewa Dangote biyan haraji ya saba ka’ida - Rafsanjani
Kungiyoyin fararen hula a Najeriya sun mayar da martani kan matakin da gwamnatin kasar ta dauka na tsawaita wa’adin shekaru biyar na dagewa kamfanin Dangote biyan haraji.
Wallafawa ranar:
A yanzu dai kamfanin na da jimillar wa’adin shekaru 10, ba tare da zai rika biyan haraji ba biyan haraji ba, yayinda gwamnatin ta ce, kamfanin zai ci gaba da gyaran hanyoyi a maimakon biyan harajin.
Sai dai yayin zantawarsa da Sashin Hausa na RFI, Auwal Musa Rafsanjani, babban darekta a wata cibiyar kare hakkin bil’adama a Najeriya ya ce, tsarin ya saba ka’ida.
A cewar Rafsanjani shekarun da aka debawa kamfanin na Dangote sun yi yawa.
Tsawaita wa’adin dagewa Dangote biyan haraji ya saba ka’ida - Rafsanjani
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu