Isa ga babban shafi
Najeriya

Mukaddashin Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Hukumar Sharia Don Gano Zargin Sojoji dake Uzurawa Jama'a

Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya kafa wani komitin bincike na musamman domin gano zarge-zargen take hakkin bil’adama da ake yiwa wasu sojan kasar.

Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo
Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo RFI
Talla

Duk da zargi da ake yiwa wasu sojan kasar na take hakkin bil’adama a chan baya, yakan kasance akan bar Hukumar sojan kasar ne su binciki kan su, kuma daga baya su wanke kan su.

Wata sanarwa daga fadar Shugaban kasa tun a jiya Juma’a na cewa Mukaddashin Shugaban kasar Yemi Osinbajo ya kafa Hukumar shari'a da ta kunshi wakilai bakwai karkashin Mai Sharia Biobele A Georgewill na kotun daukaka kara domin bin diddigin zarge-zargen da ake yiwa sojojin kasar na take hakkin bil’adama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.