Boko Haram ta kashe mutane 7 a kauyen Adamawa
Wasu da aka ce mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kai hari tare da kashe mutane 7 a kauyen Mildu da ke cikin karamar hukumar Madagali a jihar Adamawa da ke Najeriya.
Wallafawa ranar:
Rahotonni sun ce maharan sun kona gidaje da dama a lokacin harin, wanda ya zo wa jama’a da ba-za-ta lura da cewa an jima ba a kai hari a yankin ba.
Wani shaidan gani da ido, mai suna Musa, ya ce mayakan sun dau tsawon sa’a guda suna aikata barna a kauyen, kafin daga bisani mafarauta da soji sun fatatake su.
Shugaban karamar hukumar Madagali, Muhammad Yusuf, ya shaida cewa anyi nasara kashe daya daga cikin Maharan.
Harin na zuwa ne kwana guda bayan manyan hafsoshin tsaron kasar sun amsa umarni mukaddashin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo, na komawa jihar Borno don kawo karshan yaki da Boko Haram a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu